Tuesday, 6 June 2017

Image resultUwargidan Shugaban Najeriya Hajiya Aisha Buhari ta ce mijinta na murmurewa sosai kuma nan gaba kadan zai komo gida daga jinyar da yake yi a kasar Ingila.
Tana magana ne a safiyar Talata bayan da ta dawo daga London, inda ta kai masa ziyarar mako guda.
Wata guda kenan da shugaba Muhammadu Buhari, mai shekara 74, ya bar kasar zuwa Birtaniya - wacce ita ce tafiyarsa jinya karo na biyu a bana.
Hajiya Aisha ta ce shugaban ya "godewa 'yan kasar kan addu'o'in da suke yi masa da kuma goyon bayan da suke bai wa Mukaddashinsa Yemi Osinbajo".
Sai dai rashin lafiyar shugaban tana janyo ce-ce-ku-ce sosai a kasar, inda wasu ke ganin kamata ya yi shugaban ya yi murabus ya fuskanci kula da lafiyarsa.
Amma wasu kuwa suna ganin tun da ya mika ragamar shugabanci a hannun mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo, to babu wani abin damuwa.
Har yanzu dai ba a san takamaimai cutar da ke damun Shugaba Buhari ba. 

0 comments:

Post a Comment

Powered by Blogger.

Movies

Blogroll

Recent Videos

Ina samun sauki sosai — Shugaba Muhammadu Buhari

Shuagban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce yana samun sauki sosai, kuma da zarar likitoci sun ba shi dama zai koma gida domin ci gaba da ayyuk...

statistics

Search This Blog

Subscribe

Video

Recent Posts

Posts

Travel

Sample Text

Fashion

Contact Form

Name

Email *

Message *

Video Of Day

Slider

News

Games

Pages

Popular Posts