
Tana magana ne a safiyar Talata bayan da ta dawo daga London, inda ta kai masa ziyarar mako guda.
Wata guda kenan da shugaba Muhammadu Buhari, mai shekara 74, ya bar kasar zuwa Birtaniya - wacce ita ce tafiyarsa jinya karo na biyu a bana.
Hajiya Aisha ta ce shugaban ya "godewa 'yan kasar kan addu'o'in da suke yi masa da kuma goyon bayan da suke bai wa Mukaddashinsa Yemi Osinbajo".
Sai dai rashin lafiyar shugaban tana janyo ce-ce-ku-ce sosai a kasar, inda wasu ke ganin kamata ya yi shugaban ya yi murabus ya fuskanci kula da lafiyarsa.
Amma wasu kuwa suna ganin tun da ya mika ragamar shugabanci a hannun mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo, to babu wani abin damuwa.
Har yanzu dai ba a san takamaimai cutar da ke damun Shugaba Buhari ba.
0 comments:
Post a Comment