Saturday, 4 March 2017


Hukumar kare hakkin bil Adama ta Najeriya ta wanke sojojin kasar daga zargin da kungiyar Amnesty Internatioanl ta yi na cewa sojojin Najeriya na take hakkin bil Adama.
       A wani al’amari mai kama da martani ga kungiyar kare hakkin bil Adama ta Duniya Amnesty International, da a baya ta zargi sojojin Najeriya da cin zarafin bil Adama. Hukumar kare hakkin bil Adama ta Najeriya ta wanke sojojin Najeriyar.
A cewar babbar sakataren hukumar ta Najeriya, Mrs Oti Ovrawah, tace hukumar na farin cikin fadin cewa rundunar sojan Najeriya ta na la’akari da muradun kare hakkin bil Adama, a duk yake-yaken da ta keyi da ‘yan ta’adda wanda ke da muhimmanci ga ‘yan Najeriya.
Tun da farko sai da babban hafsan sojan Najeriya, Janal Tukur Buratai, yace dakarun kasar basa wani rufa-rufa game dangane da batun kare hakkin bil Adama, inda ya ci gaba da cewa basu da wani abu da zasu boye, idan aka duba ganin cewa dokokin aikin soja suna kare Muradin ‘kasa da kuma kare dukiya da rayukan jama’a ne.
Zargin da kungiyar Amnesty International ta yi wa dakarun Najeriya, ya haifar da cece-kuce a cikin ‘kasar.
Darakta janal na hukumar wayar da kan jama’a ta Najeriya, Dakta Garba Abari, na ganin abubuwan da suka faru a kasar zai zamanto darasi ne ga kungiyar Amnesty International.

0 comments:

Post a Comment

Powered by Blogger.

Movies

Blogroll

Recent Videos

Ina samun sauki sosai — Shugaba Muhammadu Buhari

Shuagban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce yana samun sauki sosai, kuma da zarar likitoci sun ba shi dama zai koma gida domin ci gaba da ayyuk...

statistics

Search This Blog

Subscribe

Video

Recent Posts

Posts

Travel

Sample Text

Fashion

Contact Form

Name

Email *

Message *

Video Of Day

Slider

News

Games

Pages

Popular Posts