Saturday, 25 March 2017

Magu

Shugaban rikon kwarya na hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa, Ibrahim Magu, ya ce wadanda ke tsoron kada a fallasu ne suke yakar sa.


A makon da ya gabata ne dai majalisar dattawan kasar ta ki amincewa da shi a matsayin tabbataccen shugaban hukumar ta EFCC.
Kuma wannan shi ne karo na biyu da majalisar ke kin tabbatar da shi.
'Yan majalisar dai na kafa hujja da cewa sun sami rahoto kan Magu daga hukumar tsaron farin kaya, DSS, ta kasar dake zarginsa.
Rahoton dai ya nuna Ibrahim Magu na da tabon laifi abin da ke sanya shakku kan yiwuwar yakar cin hanci da rashawa.

Saturday, 4 March 2017


Hukumar kare hakkin bil Adama ta Najeriya ta wanke sojojin kasar daga zargin da kungiyar Amnesty Internatioanl ta yi na cewa sojojin Najeriya na take hakkin bil Adama.
       A wani al’amari mai kama da martani ga kungiyar kare hakkin bil Adama ta Duniya Amnesty International, da a baya ta zargi sojojin Najeriya da cin zarafin bil Adama. Hukumar kare hakkin bil Adama ta Najeriya ta wanke sojojin Najeriyar.
A cewar babbar sakataren hukumar ta Najeriya, Mrs Oti Ovrawah, tace hukumar na farin cikin fadin cewa rundunar sojan Najeriya ta na la’akari da muradun kare hakkin bil Adama, a duk yake-yaken da ta keyi da ‘yan ta’adda wanda ke da muhimmanci ga ‘yan Najeriya.
Tun da farko sai da babban hafsan sojan Najeriya, Janal Tukur Buratai, yace dakarun kasar basa wani rufa-rufa game dangane da batun kare hakkin bil Adama, inda ya ci gaba da cewa basu da wani abu da zasu boye, idan aka duba ganin cewa dokokin aikin soja suna kare Muradin ‘kasa da kuma kare dukiya da rayukan jama’a ne.
Zargin da kungiyar Amnesty International ta yi wa dakarun Najeriya, ya haifar da cece-kuce a cikin ‘kasar.
Darakta janal na hukumar wayar da kan jama’a ta Najeriya, Dakta Garba Abari, na ganin abubuwan da suka faru a kasar zai zamanto darasi ne ga kungiyar Amnesty International.

Shugaba Buhari Na Shirin Dawowa Nijeriya Kafin A Rufe Filin Jirgin Sama Na Abuja

Rahotonni sun bayyana cewa wasu ma’aikatan shugaba Buhari na kokarin ganin ya shigo Nijeriya kafin a kulle babban filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja, kamar yadda majiyarmu ta Sahara Reporters ta rawaoto.
An sanar da cewa za a rufe filin jirgin ne daga ranar 7 ga watan Maris, 2017 inda zai a kai tsawon makonni shida kafin a bude.
Shugaba Buhari ya tafi kasar Ingila ranan 19 ga watan Junairu domin hutu kuma ya dawo ranan 6 ga watan Fabrairu amma har zuwa yanzu bai dawo ba bisa wasu dalilai suka nuna ceaa likitocinsa sun bukaci ya kara kwanakin hutu.
Amma an samu mishkila game da dawowar tasa, yayin da ya rubuta wasika ga majalisan dokoki cewa ba zai samu damar dawowa ba yanzu bisa ga shawarar likitoci.
Har yanzu dai masu magana da yawin shugaban kasa sun ki bayyanawa 'yan Najeriya irin cutar da shugaba Buhari ke fama da shi.
Powered by Blogger.

Movies

Blogroll

Recent Videos

Ina samun sauki sosai — Shugaba Muhammadu Buhari

Shuagban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce yana samun sauki sosai, kuma da zarar likitoci sun ba shi dama zai koma gida domin ci gaba da ayyuk...

statistics

Search This Blog

Subscribe

Video

Recent Posts

Posts

Travel

Sample Text

Fashion

Contact Form

Name

Email *

Message *

Video Of Day

Slider

News

Games

Pages

Popular Posts